\v 2 Yahweh Allah Mai kishi ne da sakayya; Yahweh mai sakayya ne da fushi mai zafi; Yahweh na ɗaukar fansa a kan abokan gãbarsa, kuma yana ci gaba da fushinsa a bisa maƙiyansa.
\v 3 Yahweh na da jinkirin fushi da iko mai girma; ba zai ƙyale miyagu ba hukunci ba. Yahweh na shirya hanyarsa a cikin guguwa da hadari, gizagizai kuma ya maishe su ƙurar tafin sawayensa.
\v 12 Ga abin da Yahweh ya faɗi, "Ko da suna cike da ƙarfinsu da kuma yawansu, duk da haka za a datse su; jama'arsu za su ƙare sarai. Amma kai, Yahuda; ko da ya ke na wahalshe ka, ba zan ƙara wahalsheka ba.
\v 14 Nineba, Yahweh ya ba da umarni game da ke; "Babu wata sauran zuriyar da za a kira ta da sunanki. Zan datse sassaƙaƙƙun gumaka da kuma gumakan ƙarfe daga gidajen allolinki. Zan haƙa kaburburanki, gama ke abin raini ce."
\v 15 Duba, a bisa duwatsu, akwai sawayen wani mai kawo labarai masu daɗi, wanda ya ke shelar salama! Yahuda, yi murnar bukukuwanka, ka kuma cika wa'adodinka, gama mugu ba zai ƙara mamaye ka ba, don an datse shi sarai.
\c 2
\cl Sura 2
\p
\v 1 Shi wanda zai daddatsa ku yana zuwa gãba da ku. Ku tsare ganuwar birnin, ku yi tsaron hanyoyi. Ku ƙarfafa kan ku, ku shirya sojojinku.
\v 3 Garkuwoyin jarumawansa jajaye ne, kuma sojojinsa sun sa jajayen tufafi, ƙarafan karusansu na walƙiya tun ranar da a ka shirya su, kuma suna karkaɗa mãsunsu masu ƙotar katako a iska
\v 5 Wanda zai daddatsa ku gutsu-gutsu ya kira jarumawansa, cikin tafiyarsu suna cin karo da juna, su na sauri don su kawo hari a kan ganuwar birnin. An shirya babbar garkuwa don ta kare masu kawo hari.
\v 8 Nineba ta zama kamar tafki mai maguda, tare da mutanenta suna gudu kamar ruwa mai kwarara. Waɗansu na ihu "ku tsaya, ku tsaya", amma ba wanda ya waiga baya.
\v 12 Zãki ya yayyaga abin da ya kama don 'ya'yansa, ya murɗe abin da ya kamo wa zãkanyarsa, ya cika kógonsa da waɗanda ya kamo, ya cika raminsa da yagaggen mushen waɗanda ya yayyaga.
\v 13 "Duba, ina gãba da ku - wannan furcin Yahweh mai runduna ne. Zan ƙone karusanku, a cikin hayaƙi, takobi kuma zai cinye ƙananan zakunanku. Zan datse ganima daga ƙasarku, kuma ba za a ƙara jin muryoyin masu kawo saƙonku ba."
\c 3
\cl Sura 3
\p
\v 1 Kaiton birni wanda ke cike da jini! Wanda ke cike da ƙarairayi da kayan sata; a kullum waɗanda aka ƙwara suna cikinsa.
\v 3 Akwai mahayan dawakai masu kawo hari, da walƙiyar takubba da ƙyallin mãsu da tarin gawaye da tsibin jukkuna. Gawarwaki ba su da iyaka; maharan sun yi tuntuɓe a kan su.
\v 4 Wannan na faruwa ne saboda mummunar sha'awa ta ayyuka kyakkyawar karuwar, ƙwararriya a maita, mai sayar da al'ummai ta wurin karuwancinta, ta wurin ta kuma mutane na aikata maitanci.
\v 5 "Duba, ina gãba da ke - wannan furcin Yahweh mai runduna ne - Zan kware zanen ki in sa ki zama tsirara a gaban al'ummai, ki zama abin kunya ga masarautu.
\v 8 Nineba, kin fi Tebes ne wadda aka gina ta kusa da Kogin Nilu, wadda ruwaye ke kewaye da ita, wadda kariyarta teku ne, wadda teku ta yi mata dajiya?
\v 10 Duk da haka an kwashe Tebes, ta tafi bauta; an fyaɗa 'ya'yanta a ƙasa a kan hanyoyi, abokan gabarta sun jefa ƙuru'u a kan manyan mutanenta, kuma an ɗaure ƙarfafan mutanenta da sarƙoƙi.
\v 15 Wuta zata same ki a wurin, takobi zai hallaka ki. Zai cinye ki kamar yadda fãra ta kan cinye komi da komi. Ki maida kanki kamar 'ya'yan fãra, ki yi yawa kamar fãrin da suka yi ƙwari sosai.
\v 17 'Ya'yan sarakunanki suna da yawa kamar fãrin da suka yi girma sosai, jarumawanki kuma na kamar fãrin da suka yi cincirindo a bango lokacin sanyi. Amma idan rana ta yi sai su tashi su tafi wurin da ba'a sani ba.
\v 19 Raunukanka ba zasu warke ba. Raunukanka sun yi zafi sosai. Dukkan wanda ya ji labarinka zai tafa hannu domin murna a kanka. Wane ne ya tserewa muguntarka ta ko yaushe?