\v 1 Wannan ita ce maganar Yahweh wadda ta zo wurin Mika, Bamorashtite a cikin kwanakin Yotam, da Ahaz, da Hezekiya, sarakunan Yahuda, abin da ya gani game da Samariya da Yerusalem.
\v 2 Dukkan jama'a ku saurara, ke duniya ki saurara da dukan abin dake cikinki. Bari Ubangiji Yahweh ya zama shaida a kan ki daga haikalinsa mai tsarki.
\v 5 Dukkan wannan saboda tawayen Yakubu ne, kuma saboda zunubin gidan Isra'ila ne. Mene ne dalilin tawayen Yakubu? Ba Samariya ba ce? Mene ne dalilin wurare masu tsawo na Yahuda? Ba Yerusalem ba ce?
\v 7 Za a farfasa sifofinta, dukkan kyaututtukanta za a ƙone su. Dukkan gumakanta zan rushe su. Gama daga wurin karuwancinta ta tattara su, zasu zama kamar abin da aka biya ta saboda karuwanci."
\v 13 Ku mutanen Lakish ku haɗa karusai na dawaki. Ke, Lakish, ke ce kika zama sanadin zunubin ɗiyar Sihiyona, saboda an sami kurakuran Isra'ila a cikinki.
\v 16 Ki aske kanki ki share gashinki saboda 'ya'yan da ki ke jin daɗin su. Ki sa kanki ya yi saiƙo kamar na gaggafa, domin 'ya'yanki za su tafi bauta daga wurinki.
\c 2
\cl Sura 2
\p
\v 1 Kaiton masu shirya mugunta, ga waɗanda ke shirya mugunta a kan gadajensu. Idan gari ya waye sukan aikata ta domin suna da iko.
\v 3 Saboda haka Yahweh yace, "Duba, na kusa kawo bala'i ga wannan kabila, wadda ba zaku cire kanku daga ciki ba. Ba zaku yi tafiya da taƙama ba, gama zaya zama mugun lokaci.
\v 4 A wannan rana abokan gãbarku zasu rera waƙa game da ku, zasu yi makoki da makoki mai zafi. Zasu yi waƙa, 'Mu Isra'ilawa mun hallaka sarai, Yahweh ya canza gundumar mutanena.' Ya ya zaya ɗauke shi daga wurina? Ya bayar da filayanmu ga maciya amana!"'
\v 7 Ko lallai za a iya faɗin gidan Yakubu, "Ko Ruhun Yahweh ya ji haushi ne?" Ko waɗannan su ne ainihin ayyukansa?" Ko kalmomina ba su yi wani aikin kirki ga kowa ba ne?
\v 8 A makare mutanena suka tashi kamar abokan gãba. Kun tuɓe sutura, da riga, daga masu wucewa ba tare da tsarguwa ba, kamar sojoji suna dawowa daga yaƙi zuwa wurin da suke tsammani lafiyayye ne.
\v 11 Idan wani ya zo da ruhun ƙarya ya yi ƙarya ya ce, "Zan yi maka anabci a kan ruwan inabi da abin sa maye," zasu ɗauke shi annabi domin wannan jama'a.
\v 12 Tabbas, zan tattara dukkan ku, Yakubu. Tabbas zan tattara sauran mutanen Isra'ila. Zan kawo su kamar garken tumaki a cikin tsakiyar wurin kiwonsu. Saboda yawan mutanen za a ji ƙara mai ƙarfi.
\v 3 ku da ke cin naman mutanena, kun yage fatarsu, kun kakkarya ƙashinsu, kun daddatsa su gunduwa-gunduwa kamar naman da za a sa a tukunya, kamar nama domin dafawa.
\v 5 Yahweh ya faɗi haka, "Game da annanbawan da suke ɓatar da mutanena, idan wani ya basu wani abu su ci, sukan yi shelar 'Salama'. Amma ga waɗanda ba su sa komi a bakinsu ba, sai su fara yaƙi da su.
\v 6 Saboda haka zai zama duhu a gare ku, babu ruya domin ku, zai zama duhu sosai har da ba zaku yi duba ba. Rana za ta faɗi a kan annabawa, yini zai yi masu duhu.
\v 11 Shugabanninku suna hukunci da cin hanci, firistocinku suna koyarwa don a biya su, kuma annabawanku suna dubã saboda kuɗi. Duk da haka kun dogara ga Yahweh kun ce, "Ba Yahweh yana tare da mu ba? Ba masifa da za ta same mu."
\v 12 Domin haka, saboda ku za a huɗe Sihiyona kamar gona, Yerusalem za ta zama juji, tudun haikali zai zama tsaunin daji.
\c 4
\cl Sura 4
\p
\v 1 Amma zaya zama a rana ta ƙarshe dutsen gidan Yahweh zaya kafu a bisa sauran duwatsu. Zai ɗaukaka bisa sauran tuddai mutane kuma za su yi tururuwa wurinsa.
\v 2 Al'ummai da yawa zasu ce, "Ku zo, mu je bisa dutsen Yahweh, zuwa gidan Allah na Yakubu. Zaya koya mana hanyoyinsa, kuma zamu yi tafiya cikin tafarkunsa." Gama daga Sihiyona shari'a zata fito, maganar Yahweh kuma daga Yerusalem.
\v 3 Shi zaya hukunta tsakanin mutane da yawa, ya kuma yanke hukunci a kan mulkoki masu yawan gaske masu nisa kuma. Zasu maida takubbansu su zama garmuna mãsun su kuma su zama lauzuna. Wata al'umma baza ta ɗaga takobi gãba da wata al'umma ba, baza su ƙara koyar da yaƙi ba.
\v 7 Zan sa guragun su zama su ne saura, waɗanda a ka kora su zama al'umma mai ƙarfi, ni kuma Yahweh zan yi mulki a bisansu, a kan Dutsen Sihiyona daga yanzu da har abada.
\v 9 Yanzu, me yasa kuke ihu da ƙarfi haka? Babu sarki a cikinku ne? Mai shawararku ya mutu ne? Wannan shi ne yasa ciwo ya kama ku kamar mace mai naƙuda?
\v 10 Ki zama da ciwo da naƙuda ta haifuwa, ke ɗiyar Sihiyona, kamar mace mai naƙuda. Gama yanzu ke zaki fita waje daga birnin, ki zauna a waje, kuma ki tafi Babila. A can za a kuɓutar da ke. A can Yahweh zaya kuɓutar da ke daga hannun abokan gãbarki.
\v 13 Tashi ki yi shiƙa ɗiyar Sihiyona, gama zan maida ƙahonki ya zama ƙarfe, kofatanki kuma su zama jan ƙarfe. Zaku hallaka mutane da yawa kuma zaku miƙa dukiyarsu ta zilama ta zama ta Yahweh, mallakarsu kuma ga Ubangijin dukan duniya."
\c 5
\cl Sura 5
\p
\v 1 Yanzu ku taru da shirin yaƙi, ɗiyan sojoji; sojoji sun yi sansani sun kewaye birni, zasu bugi alƙalin Isra'ila da sanda a kunci.
\v 2 Amma ke Betlehem Ba'ifrata, ko da yake ke ƙanƙanuwa ce a cikin dangi Yahuda, wani daga cikinki zaya zo gare ni ya yi mulkin Isra'ila, wanda farkonsa tun daga lokacin dã ne, tun daga can farko.
\v 5 Zaya zama salamarmu. Sa'ad da Asiriyawa suka shigo cikin ƙasarmu, sa'ad da suka yi gangami gãba da kagarunmu, sa'an nan zamu tashi gãba da su, makiyaya bakwai da shugabanni takwas a kan mutane.
\v 6 Zasu kiwaci ƙasar Asiriya da takobi, ƙasar Nimrod kuma a cikin ƙofofinta. Zaya kuɓutar da mu daga Asiriyawa, sa'ad da suka shiga cikin ƙasarmu, sa'ad da suka yi gangami cikin iyakokinmu.
\v 7 Waɗanda suka rage na wajen Yakubu zasu zama cikin tsakiyar mutane da yawa, kamar raɓa daga wurin Yahweh, kamar ruwa a kan ciyawa, wadda ba mutum take jira ba, ba kuma 'ya'yan mutane take jira ba.
\v 8 Waɗanda suka rage na wajen Yakubu zasu zama a cikin al'ummai, cikin mutane da yawa, kamar zãki a cikin namomin jeji masu yawa, kamar ɗan zaki a cikin garken tumaki. Sa'ad da ya shiga cikinsu zai tattaka su, ya daddatsa su, ba wanda zaya cece su.
\v 5 Mutanena, ku tuna abin da Balak sarkin Mowab ya ƙulla, da yadda Bala'am ɗan Biyo ya amsa masa sa'ad da kuke tafiya daga Shittim zuwa Gilgal, ta haka za ku san aikin adalci na Yahweh."
\v 8 Ya dai gaya maka, mutum, abin da ke mai kyau, abin da Yahweh ke nema daga wurinka: Aikin adalci, jinƙai da tafiya cikin tawali'u tare da Allahnka.
\v 14 Za ku ci ba za ku ƙoshi ba, yunwarku za ta zauna a cikinku, za ku ajiye kayayyaki amma ba za ku adana su ba, abin da kuka adana zan bayar ga takobi.
\v 15 Za ku yi shuka amma ba za ku yi girbi ba; za ku sawo zaitun amma ba za ku shafe kanku da mai ba; za ku matse kuringar inabi amma ba za ku sha ruwan ba.
\v 16 Farillan da Omri ya bayar an kiyaye su, haka kuma dukkan abin da gidan Ahab suka yi. Kun yi tafiya bisa ga shawararsu. To haka zan mai da birnin kango, mazauna ciki kuma abin ƙi, ku mazaunan za ku yi ta fama da ba'a a matsayinku na mutanena."
\c 7
\cl Sura 7
\p
\v 1 Kaito na! Gama a gare ni ya zama kamar an riga an gama girbi na kaka, har ma da kalar abin da ya rage na kuringar inabi a gonaki: Ba sauran 'ya'yan itatuwan da za a samu, babu nunar fari na 'ya'yan ɓaure waɗanda rai na ke so.
\v 2 Babu sauran amintattun mutane a ƙasar, babu sauran na kirki a cikin dukkan 'yan adam. Dukkan su sun yi kwanto domin su zãbar da jini, kowanne ɗayansu yana farautar ɗan'uwansa da tãru.
\v 3 Hannayensu sun iya yin ɓarna sosai: sarki yana nema a ba shi kuɗi, alƙali yana shirye ya karɓi cin hanci, ƙaƙƙarfan mutum yana gaya wa waɗansu abin da yake so ya samu. Haka suke rigima tare.
\v 4 Mafi kyau a cikinsu kamar laka yake, mafi aminci a cikinsu yana kamar shingen ƙaya. Dãma masu tsaronmu sun yi magana a kan wannan rana, ranar da za a hore ku. Ranar ruɗewarsu ta zo.
\v 9 Saboda na yi wa Yahweh zunubi, zan jure da fushinsa har yayi mani shari'a, yayi mani hukunci. Zai kawo ni cikin haske, zan gan shi yana kuɓutar da ni cikin adalcinsa.
\v 10 Sa'an nan maƙiyina zai gani, kunya za ta rufe wanda yake ce da ni, "Ina Yahweh Allahnka?" Idanuna zasu gan ta, za a tattake ta kamar taɓo a kan hanyoyi.
\v 12 A ranar nan mutanenka zasu zo wurinka daga Asiriya da biranen Masar, daga Masar har zuwa babban Kogi, daga teku zuwa teku, daga dutse zuwa dutse.
\v 14 Ka yi kiwon mutanenka da sandarka, garke abin gãdonka. Suna zaune su kaɗai a jeji, a tsakiyar fadama. Bari su yi kiwo a Bashan da Giliyad kamar kwanakin dã.
\v 17 Zasu lashi ƙasa kamar macizai, kamar hallittun dake rarrafe a ƙasa. Zasu fito daga cikin kogunansu da tsoro, zasu zo wurinka da tsoro, Yahweh Allahnmu, kuma za su ji tsoro saboda kai.
\v 18 Wane ne Allah kamar ka, kai da kake ɗauke zunubi, wanda yake ƙetare kurakuran mutanensa da suka rage, abin gãdonsa? Ba ka riƙe fushinka har abada, saboda kana ƙaunar ka nuna mana amincin alƙawarinka.