\v 1 Wannan ita ce maganar Yahweh da ta zo wurin Hosiya ɗan Biri a kwanakin Uziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, sarakunan Yahuda, da kuma kwanakin Yerobowam ɗan Yoash, sarkin Isra'ila.
\v 2 Sa'ad da Yahweh ya yi magana da fari ta wurin Hosiya, ya ce masa, "Jeka ka ɗaukar wa kanka mata wadda karuwa ce. Za ta sami 'ya'ya ta wurin karuwancinta. Domin ƙasar tana aikata matuƙar karuwanci ta wurin yashe da Yahweh."
\v 6 Sai Gomar ta sake yin ciki ta haifi 'ya mace. Sai Yahweh yace wa Hosiya, "Ka raɗa mata suna Lo Ruhama, gama ba zan ƙara yi wa gidan Isra'ila jinƙai ba, har da zan gafarta masu.
\v 7 Duk da haka zan yi wa gidan Yahuda jinƙai, zan cece su ni da kaina, Yahweh Allahnsu. Ba zan cece su da baka, da takobi, da yaƙi, da dawakai da mahayansu ba,"
\v 10 Duk da haka yawan mutanen Isra'ila za su zama kamar yashi a bakin teku, wanda ba za a iya aunawa ko ƙirgawa ba. Zai zamana inda aka ce masu, 'Ku ba mutanena ba ne, za a ce masu, "Ku mutanen Allah mai rai ne.'
\v 11 Mutanen Yahuda da mutanen Isra'ila za su taru wuri ɗaya. Za su naɗa wa kansu shugaba ɗaya, za su haura su tafi daga ƙasar, gama ranar Yezril zata zama da girma.
\c 2
\cl Sura 2
\p
\v 1 Ku cewa 'yan'uwanku maza, 'Mutanena!' ga 'yan'uwanku mata, 'An ji tausayin ku.'"
\v 2 Ku kawo ƙarar mahaifiyarku, ku kawo ƙara, gama ita ba matata ba ce, ni kuma ba mijinta ba ne. Ta kawar da karuwancinta daga gare ta da halinta na zina daga tsakanin nonnanta.
\v 3 Idan ba haka ba, zan maishe ta tsirara in nuna tsiraicinta kamar a ranar da aka haife ta. Zan maishe ta kamar hamada, kamar busasshiyar ƙasa, in sa ta mutu da ƙishiruwa.
\v 5 Domin uwarsu dăma karuwa ce, ita wadda ta ɗauki cikinsu ta yi abin kunya. Ta ce, "Zan bi masoyana, domin suna bani abincina, da ruwa, da ulu, da gyale, da mai da abin sha."
\v 7 Zata bi masoyanta, amma ba za ta cim masu ba. Zata neme su, amma ba za ta same su ba. Sa'annan za ta ce, "Zan koma wurin mijina na farko, gama a dã ya fiye mani da yanzu."
\v 8 Gama ba ta sani dama ni ne na ba ta hatsi ba, da sabon ruwan inabi da mai, na kuma yawaita ta da azurfa da zinariya, wanda suke amfani da shi ga Ba'al.
\v 9 Saboda haka zan karɓe hatsinta da kaka, da sabon ruwan inabina a lokacin girbi. Zan karɓe uluna da gyaluluwana da aka mora don a rufe tsiraicinta.
\v 12 "Zan lalatar da kuringar inabinta da itatuwan ɓaurenta, da ta ce, "Waɗannan su ne ladar da masoyana suka bani.' Zan maishe su jeji, namun jeji kuma za su cinye su.
\v 13 Zan hore ta domin ranakun bukukuwan Ba'aloli, lokacin da ta ƙona masu turare, sa'ad da ta yiwa kanta ado da zobba da duwatsu masu daraja, ta bi masoyanta ta manta da ni -- wannan shi ne furcin Yahweh."
\v 15 Zan mayar mata da gonakin inabinta, Kwarin Akor zai zama kofar bege. Nan za ta amsa mani kamar kwanakin ƙuruciyarta, kamar ranar da ta fito daga ƙasar Masar.
\v 18 A ranan nan zan yi alƙawari domin su da namun jeji, da tsuntsayen sama, da masu rarrafe a ƙasa. Zan kori bakã, da takobi, da kuma yaƙi daga ƙasar, in sa ku zauna lafiya.
\v 23 Zan dasa ta domin kaina a ƙasar, zan nuna jinkai akan Lo Ruhama, Zan cewa Lo Ammi, 'Ke ce Ammi Attah,' sa'annan za su ce mani, 'Kai ne Allahnmu."'
\c 3
\cl Sura 3
\p
\v 1 Yahweh yace mani, "Jeka har wa yau, ka ƙaunaci wata mata wadda kaunatacciya ce ga mijinta, amma mazinaciya ce. Ka ƙaunaceta kamar yadda Ni, Yahweh, na ke ƙaunar mutanen Isra'ila, ko da yake sukan juya zuwa ga bin waɗansu alloli, suna ƙaunar wainar 'ya'yan itatuwa."
\v 4 Gama mutanen Isra'ila za su kasance kwanaki da yawa ba sarki, ba kuma ɗan sarki, ba hadaya, ba bagadin dutse, ba falmara ko gumakan gida.
\v 5 Daga baya mutanen Isra'ila za su juyo su nemi Yahweh Allahnsu da sarkinsu Dauda, kuma a kwanakin ƙarshe, za su zo da rawar jiki gaban Yahweh da alheransa.
\c 4
\cl Sura 4
\p
\v 1 Ku ji maganar Yahweh, ku mutanen Isra'ila. Yahweh yana da ƙara game da mazaunan ƙasar, domin babu gaskiya ko alƙawarin aminci, babu sanin Allah a ƙasar.
\v 3 Saboda haka ne ƙasar take bushewa, dukkan mazaunanta kuma suna yanƙwanewa; dabbobin jeji da tsuntsayen sama, har ma da kifayen dake a teku, ana kawar dasu.
\v 6 Ana hallaka mutanena saboda rashin ilimi. Saboda ku firistoci kun ƙi ilimi, nima zan ƙi ku zama firistocina. Domin kun manta da dokokina, ko da yake ni Allahnku ne, nima zan manta da 'ya'yanku.
\v 12 Mutanena suna neman shawara daga gumakun itacensu, sandar tafiyarsu kuma na basu anabce - anabce. Domin tunanin fasiƙanci ya ɓadda su, sun aikata karuwanci maimakon su zama da aminci ga Allahnsu.
\v 13 Suka miƙa hadayu a ƙwanƙolin duwatsu, suka ƙona turare bisa tuddai, ƙarƙashin rimaye, foflas da tsamiya, domin inuwar tana da daɗi. Sai 'ya'yanki mata suka yi lalata, surukanki mata kuma suka yi zina.
\v 14 Bazan hori 'ya'yanki mata ba sa'ad da suka zaɓi suyi fasiƙanci, ko surukanki mata idan suka yi zina. Domin maza ma suna bada kansu ga karuwai, suna miƙa hadayu domin su yi lalata da keɓaɓɓun karuwai. Waɗannan mutane da basu da ganewa zan fyaɗa su ƙasa.
\v 15 Koda yake Isra'ila kin yi zina, bari Yahuda ma kada ta yi saɓo. Ku mutane, kada ku tafi Gilgal, kada ku haye zuwa Bet Aben, kada kuma ku rantse kuna cewa, "Yahweh hakika mai rai ne."
\v 19 Iska za ta nannaɗe ta cikin fukafukanta; za su kuma ji kunya saboda hadayunsu.
\c 5
\cl Sura 5
\p
\v 1 Ku ji wannan ku firistoci! Ku natsu, gidan Isra'ila! Ku kasa kunne, gidan sarki! Domin hukunci na zuwa bisa kanku dukka. Kun zama tarko a Mizfa tarun da aka baza akan Tabor.
\v 13 Da Ifraim ya ga cutarsa, Yahuda ma ya ga rauninsa, sai Ifraim ya tafi Asiriya, Yahuda kuwa ya aiki jakadu wurin babban sarki. Amma bai iya warkar da mutanen ku ba, bai kuma iya warkar da raunukanku ba.
\v 14 Saboda haka zan zama kamar zaki ga Ifraim, kuma kamar dan zaki ga gidan Yahuda. Ni, I, Ni' kaina zan kekketasu in yi tafiya ta; zan kwashe su; ba kuma wanda zai cecesu'
\v 3 Bari mu san Yahweh, bari mu ƙara nacewa mu san Yahweh. Zuwansa tabbataccene kamar wayewar gari. Zai zo wurinmu kamar ruwan sama, kamar ruwan ƙarshe mai jiƙa ƙasa.
\v 9 Kamar yadda taron mafasa suke wa mutum kwanto haka ƙungiyar firistoci suke haɗa kai su yi kisa a hanya zuwa Shekem; sun aikata laifofi masu ban kunya.
\v 11 Ke kuma, Yahuda, an ƙaddara miki girbi, sa'ad da zan mayar wa mutanena albarkunsu.
\c 7
\cl Sura 7
\p
\v 1 Duk lokacin da nake so in warkar da Isra'ila, sai zunuban Ifraim su bayyana, haka kuma mugayen ayyukan Samariya, domin suna shirya yaudara; ɓarawo ya kan shigo, mafasa kuwa su kai hari a titi.
\v 14 Basu yi mani kuka da dukkan zuciyarsu ba, amma a kan gadajensu suke rusa kuka. Suna taruwa domin hatsi da sabon ruwan inabi, sun juya daga gareni.
\v 16 Sun dawo, amma ba su dawo wurina ba, Mafi Ɗaukaka. Suna kama da bakan da ya saki. Hakimansu za su fãɗi da kaifin takobi, saboda hasalar harshensu. Wannan zai jawo masu ba'a cikin kasar Masar.
\v 4 Sun naɗa sarakuna, amma ba dani ba, sun yi hakimai, amma bada sani na ba. Da zinariyar su da azurfa suka yi wa kansu gumakai, amma lallai za a datse su."
\v 13 Game da maganar hadayun baye-bayena, suna hadaya da nama su kuma ci. Amma ni, Yahweh, ban karɓe su ba. Yanzu zan tuna da muguntarsu in hukunta zunubansu. Za su koma Masar.
\v 14 Isra'ila ya manta da ni, Mahaliccinsa, ya kuma gina masarautai. Yahuda ya gina garu masu yawa, amma zan aikar da wuta bisa biranen su; zai hallakar da kagara.
\c 9
\cl Sura 9
\p
\v 1 Isra'ila, kada ka yi farinciki, tare da murna kamar sauran mutane. Gama ka yi ta rashin aminci, ka yashe da Allahnka. Kana son biyan haƙƙoƙin karuwa a dukkan masussukai.
\v 4 Ba zasu zuba hadayun inabi ga Yahweh ba, ba kuma zasu zama abin karɓa gare shi ba. Hadayunsu zasu zama kamar abincin makoki: duk wanda ya ci shi zai ƙazantu. Domin abincinsu zai zama nasu ne kaɗai; ba zai zo cikin gidan Yahweh ba.
\v 6 Gama, duba, idan sun kubcewa hallaka, Masar zata tara su, Memfis kuma za ta bizne su, kayayyakin daraja na azurfa - abubuwa masu tsini zasu mallake su, ƙayayuwa kuma za su cika rumfunansu.
\v 10 Yahweh yace, "Lokacin da na samo Isra'ila, kamar samun 'ya'yan inabi ne a cikin jeji. Kamar nunan farin itacen ɓaure a lokacinsa, na samo ubanninku. Amma suka je wurin Ba'al Fiyo, suka kuma miƙa kansu ga wannan gunki abin kunya. Suka zama abin ƙyama kamar gunkin da suke ƙauna.
\v 15 "Saboda muguntarsu a Gilgal, a can ne na fara ƙinsu. Saboda mugayen ayyukansu, zan kore su daga cikin gidana. Bazan ƙara ƙaunarsu ba; dukkan shugabanninsu 'yan tawaye ne.
\v 17 Allahna zai ƙi su saboda ba suyi masa biyayya ba. Zasu zama masu kai wa da komowa cikin al'ummai.
\c 10
\cl Sura 10
\p
\v 1 Isra'ila kuringa ce mai yabanya dake ba da 'ya'yansa. Gwargwadon yawan 'ya'yansa gwargwadon yawan gina bagadansa. Bisa ga albarkar ƙasarsa, yakan inganta ginshiƙansa.
\v 4 Maganganunsu na wofi ne, su kan ɗauki wa'adodi ta wurin rantsewa kan ƙarya. Domin wannan adalci ya tsuro kamar tsire - tsire masu dafi cikin gona.
\v 5 Mazaunan Samariya zasu tsorata saboda 'yan'maruƙan Bet Aben. Mutanenta zasu yi makoki a kanta, kamar yadda mazinatan firistoci suka yi murna a kansu da darajarsu, amma yanzu ba su nan.
\v 8 Za a hallakar da wurin zaman mugunta. Wannan shi ne zunubin Isra'ila! Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya zasu fito bisa bagadansu. Mutane zasu cewa duwatsu, "Ku rufe mu!" tuddai kuma, "Ku faɗo mana!"
\v 11 Ifraim horarriyar karsana ce dake son sussukar hatsi, zan sa karkiya a bisa kyakkyawan wuyanta. Zan sa karkiya a wuyan Ifraim; Yahuda zai yi huɗa; Yakubu kuma zai ja garma da kansa.
\v 12 Ku shuka wa kanku adalci, za ku girbi ɗiyan alƙawarin aminci. Kuyi kaftun saurar ƙasarku, gama lokaci ya yi da za a nemi Yahweh, har lokacin da zai zo ya zuba adalci a kanku.
\v 14 Domin wannan hargitsin yaki zai tashi daga cikin mutanenku, za a kuma lalatar da dukkan garuruwanku masu kagara, zai za ma kamar yadda Shalman ya lalatar da Bet Arbel a ranar yaƙi, aka datse uwaye da 'ya'yansu gunduwa-gunduwa.
\v 8 Ta yaya zan iya rabuwa da kai, ya Ifraimu? Ta yaya zan mika ka, ya Isra'ila? Ƙaƙa zan maishe ka kamar Adma? Yaya zan maishe ka kamar Zeboyim? A gare ni zuciyata ta canza; dukkan jinƙaina ya harzuƙa.
\v 9 Bazan tabbatar da zafin fushina ba; bazan hallakar da Ifraim ba. Gama Ni Allah ne ba mutum ba; Ni ne Mai Tsarki wanda ke tsakiyar ku, ba kuwa zan zo cikin hasala ba.
\v 12 Ifraim ya kewaye ni da ƙarairayi, gidan Isra'ila kuma da yaudara. Amma Yahuda har yanzu yana tare da ni, Allah, yana yi mani aminci, Mai Tsarkin nan."
\c 12
\cl Sura 12
\p
\v 1 Ifraim yana ci daga iska, ya na bin iskar gabas. Kullum yana yawaita ƙarairayi da ta'addanci. Sun yi alƙawari da Asiriya suna ɗaukar man zaitun zuwa Masar.
\v 8 Ifraim yace, "Hakika na zama mai arzaƙi sosai; na samarwa kaina dukiya. A cikin dukkan aikina ba za a sami laifi a ciki na ba, ko duk wani abin da zai zama zunubi."
\v 11 Idan akwai mugunta a Giliyad, hakika mutane sun zama marasa amfani. A Gilgal sun yi hadayar bajimai; bagadansu zasu zama kamar tsibi -tsibin dutse a cikin gonaki.
\v 2 Yanzu, sai ƙara zunubi suke tayi, suna yiwa kansu sifofi na zubi daga azurfarsu, gumaka ne da masu hikima suka ƙera, dukkan su aikin gwanayen masu sana'a ne. Mutane suka ce masu, 'Waɗannan mutane masu miƙa hadaya sunyiwa 'yanmaruƙa sumba.'
\v 4 Amma ni ne Yahweh Allahnka tun daga ƙasar Masar, dole ka sani cewa ba bu wani Allah sai ni, dole kuma ka amince cewa banda ni babu wa ni mai ceto.
\v 8 Zan faɗa masu kamar damisa da aka ƙwace mata 'ya'yanta, zan tsaga haƙarƙarin ƙirjin su, a can ne zan cinye su kamar zaki, kamar naman jeji zan yayyage su gunduwa-gunduwa.
\v 14 ̀̀̀̀̀Zan cece su daga hannun Lahira? Zan cece su daga mutuwa? Mutuwa, ina, annobanki? Lahira, ina hallakarwarki? Babu sauran tausayi daga idanuna."
\v 15 Koda Ifraim ya azurta cikin 'yan'uwansa, iskar gabas za ta zo; guguwar Yahweh za ta buga daga hamada. Maɓulɓular Ifraim za ta bushe, rijiyarsa ba zata ba da ruwa ba. Abokan gãbarsa zasu washe ɗakin ajiyar dukkan kayansa masu daraja.
\v 16 Samariya za ta ji kunya, domin ta tayarwa Allahnta. Zasu faɗi ta kaifin takobi; ƙananan 'ya'yansu za a yayyankasu, matansu masu ciki za a farke su.
\c 14
\cl Sura 14
\p
\v 1 Isra'ila, ka juyo wurin Yahweh Allahnka, gama ka faɗi saboda laifinka.
\v 2 Ka ɗauki maganganun tare da kai ka juyo wurin Yahweh. Ka ce masa, "Ka kawar da dukkan laifinmu ka kuma karɓi abin da ke mai kyau, domin mu iya miƙa maka ɗiyan leɓunanmu.
\v 3 Asiriya ba za su cece mu ba; ba za mu hau dawakai mu yi yaƙi ba. Ba kuwa zamu ƙara ce da aikin hannuwanmu, 'Ku ne allolinmu,' gama a cikinku marayu ke samun jinƙai."
\v 8 Ifraim, me zan yi kuma da gumaka? Zan amsa masa in lura da shi. Ni kamar itacen bakin rafi ne wanda kullum ganyayensa kore ne; daga wurina kuke samun 'ya'ya."
\v 9 Wane ne mai hikima da zai fahimci waɗannan abubuwa? Wane ne ya fahimci waɗannan abubuwa domin ya san su? Gama hanyoyin Yahweh dai-dai suke, adali kuwa zaya yi tafiya cikinsu, amma masu tayarwa zasu faɗi a cikinsu.